Wani fitaccen dan gwagwarmaya kuma mai rajin kare hakkin masu bukata ta musamman, Injiniya Abdul Haruna, ya bukaci gwamnatin tarayya da ta dauki matakan gaggawa wajen kare hakkin masu fama da lalurar laka a Najeriya, tare da kafa sabuwar doka da za ta kula da bukatunsu na musamman.

Injiniya Haruna, wanda ya taba shugabantar kungiyar masu lalurar laka a Najeriya (SCIAN), reshen Kano, ya bayyana haka cikin wata takarda da ya fitar a ranar Asabar, inda ya jaddada bukatar kulawa ta musamman da wannan rukuni ke bukata.
A cewarsa, akwai bukatar saka masu fama da wannan lalura a cikin kundin tsarin mulkin kasa da samar da sabuwar doka da za ta fayyace hakkokinsu da hanyoyin da gwamnati za ta tallafa musu. Ya ce:
“Ko da yake ana kiran su masu bukata ta musamman, amma lalurar laka na da matukar bukatar kulawa ta daban, kama daga magani, sake farfaɗowa har zuwa tallafin zamantakewa.”
Haruna ya bayyana cewa a jihar Kano kadai, sama da mutane 4,000 ne ke samun lalurar laka a kowace shekara — mafi yawanci sakamakon hadurran ababen hawa — lamarin da ya bukaci kulawa daga matakin gwamnatin tarayya.
Muhimman Shawarwarin Haruna:
- Kafa sabuwar doka a shekarar 2025 da za ta halasta gina cibiyoyin jinya a sassa daban-daban na kasa.
- Kafa Hukumar Kula da Masu Lalurar Laka ta Kasa (NSCIC) domin lura da shirye-shirye da kuma gudanar da bincike kan matsalolin da suka shafi masu fama da raunin kashin baya.
- Samar da Tsarin Dabarun Kulawa da Masu Lalurar Laka na Ƙasa, domin tsara manufofi da hanyoyin aiwatar da su a dogon lokaci.
Baya ga haka, ya bukaci:
- Gina cibiyoyin jinya ta musamman (rehabilitation centers) a kowace yanki shida na siyasa a kasar nan, wadanda za su kasance da kayan aiki irin su na tiyata, motsa jiki, kulawar kwakwalwa da koyar da sana’o’i.
- Saka magungunan masu lalurar laka cikin tsarin inshorar lafiya ta kasa (NHIS) domin sauƙaƙe samun su da rage kudinsu.
- Ilmantar da masu lalura da iyalansu, da samar musu da horon sana’a da damar samun ayyukan yi da tallafin kasuwanci.
Bukatar Wani Tsari Mai Dorewa
Haruna ya kuma bukaci gwamnati ta tabbatar da cewa duk gine-gine da hanyoyin sufuri sun dace da bukatun masu nakasa, tare da wayar da kan al’umma domin rage wariya da kyamar masu fama da wannan lalura.
Don ƙarfafa fahimta da hadin kai, ya bada shawarar a ayyana 5 ga Satumba a matsayin Ranar Wayar da Kan Jama’a Game da Masu Lalurar Laka a Najeriya.
Kira Ga Doka da Kariya
A ƙarshe, Injiniya Haruna ya bukaci karfafa dokokin hana wariya a fannoni kamar ilimi, lafiya da ayyukan yi. Ya ce hakan zai taimaka wajen bai wa masu fama da lalurar laka damar rayuwa cikin martaba, walwala da cikakken shiga cikin al’umma.
“Wannan yunƙuri ba wai don lafiya kadai ba ne, amma domin dawo da martabar rayuwa da tabbatar da cewa waɗanda ke fama da wannan lalura na da cikakkiyar damar kasancewa cikin al’umma kamar kowa.”